An yi jana'izar mutum takwas da ƴan bindiga suka kashe a Katsina

top-news

An yi jana'izar mutum takwas da ƴan bindiga suka kashe a wani hari da suka kai karamar hukumar Jibia na jihar Katsina.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa mutum huɗu sun jikkata, sannan ba a ga guda wasu biyu ba a harin da aka kai a ranar Lahadi da dare

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa ƴan bindigar sun zo da yawa inda suka far wa mutanen waɗanda ke kan hanyarsu ta komawa gida daga kauyen Kukar Babangida zuwa Ƴan Gayya.

Mutumin ya bayyana cewa waɗanda aka kashe ba su haura shekaru 22 zuwa 47 kuma dukkansu ‘yan kauyen Yan Gayya ne.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Abubakar Sadiq, shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin.

Jibia dai na kan iyakar Najeriya da Nijar. Karamar hukumar ta kuma yi iyaka da kananan hukumomin Batsari, Kaita, Katsina, Batagarawa da kuma Zurmi.
BBC Hausa

NNPC Advert